Isa ga babban shafi
DR Congo

Shirin sasanta rikicin Jamhuriyyar Demokradiyar Congo ya ci tura

Kokarin cimma matsaya tsakanin gwamnatin Jamhuriyyar Demokaradiyar Congo da 'yan adawa don ganin an bar Shugaba Joseph Kabila ya ci gaba da mulki ya ci tura, ganin zaman da bangarorin biyu suka kwashi dogon lokaci suna yi ya gagara samar da mafita.

Joseph Kabila, Shugaban Jamhuriyyar Kongo mai son zarcewa da mulki.
Joseph Kabila, Shugaban Jamhuriyyar Kongo mai son zarcewa da mulki. © AFP PHOTO / CARL DE SOUZA
Talla

Masu shiga tsakani sun yi fatan warware matsalar kafin soma bukukuwan krismeti gudun kada rikicin kasar ya rikide zuwa yakin basasa.

Rahoton Majalisar Dinkin Duniya ya nuna cewa mutane arba’in ne suka mutu a rikicin da ya barke bayan da shugaba Kabila ya ki amincewa da sauka daga karagar mulki bayan da wa’adin mulkinsa ya shude.

Shugaba Joseph Kabila dai ya ci gaba da zama a karagar mulki duk da cewa kudurin dokar kasar bai ba shi damar sake neman mulki a wa'adi na uku ba.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.