Isa ga babban shafi
Libiya

An kwashe sinadaran hada makami mai guba daga Libya

Hukumomin kasar Libya sun ce an kwashe kaso na karshe na sinadarin hada makami mai guba daga kasar a karkahsin shirin Majalisar Dinkin Duniya.

Firaministan gwamnatin Libya mai samun goyon bayan Majalisar Dinkin Duniya Fayez Seraj
Firaministan gwamnatin Libya mai samun goyon bayan Majalisar Dinkin Duniya Fayez Seraj REUTERS
Talla

Wani jami’in tsaron kasar ya shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa cewar, cikin sinadarin da aka kwashe akwai tankuna 23 na siandarin da aka aika da shi kasar Jamus a jirgin ruwan Denmark.

Mataimakin Firaministan kasar Mussa el-Koni ya tabbatar da kwashe sinadaran.

Batun yunkurin mallakar makami mai guba yana daya daga cikin dalilan da suka kara tsamin dangantaka tsakanin tsohon shugaban Libiya marigayi Mu'ammar Gaddafi a waccan lokaci da kuma turawan yamma.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.