Sojan Libya sun kai hare-hare sansanonin 'yan kungiyar
Dakarun Gwamnatin kasar Libya sunyi ta wutan bama-bamai wasu sansanoni na ‘yan kungiyar IS dake garin Sirte, inda ake ta kai hare-hare ta sama, domin Soja su shiga garin ta kasa don kwace yankin daga hannun kungiyar.
Wallafawa ranar:
Reda Issa kakakin Gwamnatin Hadin Kai na Libya ya shaidawa kamfanin Dillancin labaran Faransa AFP cewa yau Alhamis sojan suka kai wannan hari.
Ya bayyana cewa Sojoji injiniyoyi na kokarin share nakiyoyi da aka daddasa a hanyoyin shiga garin na Sirte
Idan har akayi nasarar kwace garin Sirte daga hannun ‘yan kungiyar IS zai kasance babbar nasara ga Gwamnatin Libya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu