Isa ga babban shafi
Habasha

An yi zanga-zangar adawa da gwamnatin Habasha

Jami’an ‘yan sandan Habasha sun kama mutane da dama a wata zanga-zangar adawa da gwamnatin kasar da suka gudanar a birnin Addis Ababa a wannan asabar.

An kama masu zanga-zangar adawa da gwamnatin Habasha a birnin Addis Ababa
An kama masu zanga-zangar adawa da gwamnatin Habasha a birnin Addis Ababa REUTERS/Tiksa Negeri
Talla

Kungiyoyin ‘yan adawa daga gungun kabilun Oromo da ke da yawan al’umma ne suka shirya zanga-zangar, inda mutane kimanin 500 suka yi gangamni a dandalin Meskel tare da fadin cewa, suna bukatar gwamnati ta basu ‘yancinsu, sannan kuma ta sake musu ‘yan siyasar da aka garkame a gidan-kaso.

A ranar juma'a ne  Firaministan kasar Haile Mariam Dessalegn ya haramta gudanar da zanga-zangar wadda ya bayyana a matsayin baraza ga zaman lafiyar kasar ta Habasha.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.