Isa ga babban shafi
FRANCE- CAR

Faransa Ta Kori Soja Biyar Saboda Hannu Wajen Ayyukan Hashsha a Janhuriyar Africa

Kasar Faransa ta hukunta wasu sojan kasar biyar wadanda ke da hannu wajen cin zarafin mutane yayin da suke aikin wanzar da zaman lafiya a kasar Janhuriyar Africa ta Tsakiya. 

Shugaban kasar Africa ta Tsakiya Faustin-Archange Touadéra tare da Shugaban Faransa Francois Hollande
Shugaban kasar Africa ta Tsakiya Faustin-Archange Touadéra tare da Shugaban Faransa Francois Hollande REUTERS/Jacky Naegelen
Talla

Ma'aikatar Tsaro ta Faransa ta sanar da daukan wannan hukunci yau Asabar.

Ma'aikatar ta fadi cewa saboda girman zargin da ake yiwa sojan an dakatar dasu, kuma za’a dauki wasu matakan ladabtarwa da koran kare daga aikin sojan kasar Faransa.

Kasar Faransa ta jagoranci tura sojan ta zuwa kasar Janhuriyar Africa ta Tsakiya domin aikin wanzar da zaman lafiya, bayan barkewar rikicin kabilanci da na addini da yayi sanadiyyar mutuwar dimbin mutane a kasar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.