Sojoji sun gano babbar cibiyar da ‘Yan Boko Haram ke hada Bom
Rundunar Sojin Najeriya ta ce ta gano wata cibiya da kungiyar Boko Haram ke hada bama bamai da abubuwa masu fashewa a garin Ngala cikin Jihar Borno yankin arewa maso gabashi.
Wallafawa ranar:
Kakakin rundunar Sojin Kanal Usman Kukasheka ya ce sojojinsu sun gano tunkunyar gas kusan guda 20 manya da kanana a cikin cibiyar hada abubuwan masu fashewa.
Sannan sojojin sun samu abubuwa da dama da ake amfani da su wajen hada bama bamai a cikin cibiyar ta yan Boko Haram a Ngala.
Kanal Usman ya ce sun gano inda ‘Yan Boko Haram ke hada bama baman ne daga bayanan sirrin da suka samu, sannan sun tarwatsa cibiyar tare da kashe ‘Yan Boko Haram.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu