Tsohon Gwamnan Bauchi ya fice daga PDP
A Najeriya tsohon Gwamnan jihar Bauchi Mallam Isa Yuguda yayi shelar ficewa daga jam’iyyar sa ta asali wato PDD ,jam’iyyar da ya kasance Gwamna a karkashin ta na tsawon kusan shekaru 8.
Wallafawa ranar:
Isa Yuguda da ya sauka daga kujerar Gwamna a bara ya bayyana cewa ba ya tunanin shiga wata jam’iyya a halin yanzu, kuma ya bar jam’iyyar PDP ne bisa abinda ya kira kazantar dake cikin ta.
Jam’iyyar ta PDP na ci gaba da fuskantar matsalloli tun bayan zaben shugabancin kasar ,inda dan takara a jam’iyyar tsohon Shugaban kasar Goodluck Ebele Johnatan yayi kasa a guiwa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu