Nigeria da China Sun Kulla Muhimman Yarjeniyoyi Shida
Nigeria za ta shigar da kudaden kasar China cikin kudaden ta na asusun waje, a ci gaba da tabbatar da dorewar zumunci tsakanin ta da kasar China.
Wallafawa ranar:
A nahiyar Africa, Nigeria za ta kasance kasa ta farko da ta shigar da kudaden kasar China cikin kudaden da take dasu a waje.
Wannan na daga cikin yarjeniyoyi shida da Shugaban China Xi Jinping da Shugaban Nigeria Muhammadu Buhari suka sanya hannu ciki, a birnin Beijing.
Shugabannin biyu sun sanya hannu cikin yarjejeniya da suka hada da harkokin masana’antu, sufurin jiragen sama da harkokin samar da muhimman bukatu na jama’a.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu