Isa ga babban shafi
Afrika ta Tsakiya

Majalisar Dinkin Duniya ta yaba da zaben da aka yi a Afrika ta Tsakiya

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Ban Ki Moon ya yaba da yadda aka gudanar da zaben shugaban kasar Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya cikin kwanciyar hankali, inda ya bukaci shugabannin kasar da su tabbatar da dorewar zaman lafiya.

Faustin-Archange Touadéra sabon Shugaban kasar Afrika ta Tsakiya
Faustin-Archange Touadéra sabon Shugaban kasar Afrika ta Tsakiya REUTERS/Siegfried Modola
Talla

Ban wanda ya aike da sakon taya murna ga Faustin-Archange Touadera sakamakon nasarar da ya samu kamar yadda rahotanni suka nuna, yace nasarar zata bada damar ci gaba da sasanta tsakanin bangarorin da basa ga maciji da juna.

Touadera wanda tsohon malamin jami’a ne kuma tsohon Firaminista ya samu kashi 60 na kuri’un da aka kada.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.