Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya

An dan samu lafawar tashin hankali a Bangui na kasar Afrika ta tsakkiya

A jiya Assabar a dan samu lafawar tashin hankali a birnin Bangui babban birnin Jamhuriya Afrika ta Tsakkiya, bayan taho mugamar tsawon kwanaki 4 da aka share ana yi a birnin,

Les Forces des Nations unies patrouillent dans les rues de Bangui, suite aux violences de mercredi, le 8 octobre 2014.
Les Forces des Nations unies patrouillent dans les rues de Bangui, suite aux violences de mercredi, le 8 octobre 2014. AFP/PACOME PABAMDJI
Talla

Yanzu haka dai shugabar gwamnatin rikon kwaryar kasar Uwargida Katrin Samba Panza na ta fafatukar tattaunawa da shuwagabannin kungiyar mayakan sa kai Kristoci makiya musulunci da musulmi a kasar (Anti Balaka), da nufin samar da kwanciyar hankali mai dorewa a wannan kasa.

Tashin hankalin da ya wakana dai shine irinsa mafi muni da aka gani tun karshen watan Ogustan da ya gabata a birnin na Bangui, wanda ya yi sanadiyar mutuwar a kalla mutane 10, da suka hada da wani sojan samar da zaman lafiya na Majalisar DD dan kasar Pakistan guda, da aka kashe a ranar alhami, a yayin da wasu da dama daga cikin dakarun na duniya suka samu raunuka
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.