Isa ga babban shafi
Najeriya-Turai-Libya

Buhari ya gargadi Turai kan Libya

Shugaban Kasar Najeriya Muhammadu Buhari ya bukaci kasashen duniya dasu taimaka wajen kawo karshen rikicin kasar Libya, inda yayi gargadi cewa yana iya shafar sauran kasashen Africa dama Turai.

Shugaban Kasar Najeriya Muhammadu Buhari yayin gabatar da jawabi a zauran Majalissar Turai a Strasbourg, France.
Shugaban Kasar Najeriya Muhammadu Buhari yayin gabatar da jawabi a zauran Majalissar Turai a Strasbourg, France. REUTERS/Vincent Kessler
Talla

Muhammadu Buhari dake magana a Strausbourg na kasar Faransa a jawabinsa daya gabatar gaban wakilan majalisar kasashen Turai yace yadda abubuwa ke tafiya musamman a kudancin Libya na da ban tsoro domin hatta Najeriya ba ta tsira ba, kasancewa makamai dake shiga Najeriyan daga kasar Libya ake kaisu.

Kungiyar Kasashen Turai da Majalisar Dinkin Duniya na goyon bayan ganin a kafa Gwamnatin hadaka ne akasar Libya.

Tun a shekarar 2014 kasar Libya ke karkashin Jagoranci Gwamnatoci biyu da ‘yan majalissar dokoki, inda amintacciyar gwamnatin kasar ga kasashen duniya ke da shedikwata a gashin birnin Tobruk, yayin da daya bangaren gwamnati ta ‘yan tawaye ke zamanta a Tripoli.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.