Burundi
Amurka ta bukaci ‘Yan kasarta su fice Burundi
Gwamnatin kasar Amurka ta umurci ‘Yan kasarta su gaggauta ficewa Burundi saboda rikicin kasar da ke ci gaba da kazancewa.Wannan na zuwa ne bayan mutuwar mutane 90 a rikicin da ya faru a ranar Juma’a a Bujumbura.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Talla
Mai Magana da yawun sojan kasar Gaspard Baratuza ya fadi cewa wasu ‘yan bindiga ne suka kai hari a wurare uku na barikicin Sojoji, inda aka kashe 79 tare da kame wasu 45.
Kisan shi ne mafi muni tun bayan da shugaban kasar Pierre Nkuruziza ya zarce da mulkin kasar wa’adi na uku da karfin tsiya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu