Tunisia
Bam ya hallaka Jami’an tsaron Fadar Gwamnatin Tunisia
Wani bam da aka jefa kan tawagar jami’an tsaron da ke gadin shugaban kasar Tunisia ya hallaka mutane 14 kana wasu 11 sun samu raunuka.
Wallafawa ranar:
Talla
Kakakin fadar shugaban kasar Moez Zinaoui ya ce an kai harin ne a kan titin Shugaba Muhammed na 5 a birnin tunis kan Mota kirar bus da Jami'an tsaron ke ciki.
Kasar Tunisia na fuskantar hare-haren ta’adanci tun shekarar 2011, kuma kawo yanzu babu wanda ya dau alhakin wannan harin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu