Isa ga babban shafi
Burundi

MDD za ta tura dakaru Burundi saboda rikicin kasar

Majalisar Dinkin Duniya na wani shirin gaggawa don tura dakarun samar da zaman lafiya daga Jamhuriyar Demokiradiyar Congo zuwa Burundi don magance tashe tashen hankulan da ake ci gaba da samu a kasar. 

Mutane da dama sun rasu a rikicin siyasar Burundi
Mutane da dama sun rasu a rikicin siyasar Burundi REUTERS/Goran Tomasevic
Talla

Matakin na gaggawa na zuwa ne a daidai lokacin da Majalisar ke bayyana damuwarta kan yadda kasar ke neman fada wa cikin rikici irin wanda aka gani a Rwanda.

Jami’in Majalisar ya ce wannan ne ya sa za su tura sojojin Majalisar da ke Congo zuwa Burundi a matsayin matakin farko.

Tun bayan da shugaba Pierre Nkurunziza ya bayyana aniyarsa ta yin wa’adi na uku, kasar Burundi ta fada cikin rikicin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane 252, kana sama da mutane 200,000 sun gudu sun bar kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.