Marie-Madeleine N’kouet Shugabar hukumar zaben Africa ta Tsakiya
An nada Marie-Madeleine N’kouet a matsayin sabuwar shugabar hukumar zaben Jamhuriyar Afrika ta tsakiya, wadda kafin nan take rike da mukamin babbar magatakarda a hukumar zaben.
Wallafawa ranar:
Da farko dai an tsara gudanar da zaben raba gardama kan sabon kundin tsarin mulkin kasar ne a ranar 4 ga wannan wata na okotoba, to sai dai sakamakon tashe-tashen hankula, ya sa aka dage zaben shugaban wanda shi ma ya kamata a yi a ranar 18 ga wannan wata na oktoba.
kungiyar kasashen Africa ta AU na ci gaba da yi kira zuwa masu ruwa da tsaki a wannan rikici na gani sun cimma matsaya,kawo karshen rikicin ne zai taimakawa wajen dawowa da kwantiar hankali mai dorewa a kasar ta Afrika ta Tsakiya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu