Yan Tawayen Seleka na shirin zuwa birni Bangui
Dakarun Majalisar Dinkin Duniya sun kaddamar da wani aiki dan hana tsoffin yan Tawayen Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya yin takakkiya zuwa birnin Bangui.
Wallafawa ranar:
Rahotanni sun ce anyi ta jin karar bindigogi masu sarrafa kan su a garin Sibut dake Arewacin Bangui, lokacin da sojojin suka tare mayakan da suka fito daga Kaga bandoro.
Su dai yan tawayen Seleka sun sha alwashin isa birnin na Bangui.
Dakarun kasar Faransa na ci gaba da sutunri a wasu muhiman wurare a Birni Bangui, ya zuwa yanzu Uwargida Catherine Samba Panza shugabar Gwamnatin wucen gadin kasar ta yi kira zuwa yan kasar da su kaucewa tada tarzoma.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu