Isa ga babban shafi
Burundi

Nkurunziza ya bayar da wa'adin ajiye makamai a Burundi

Shugaban Kasar Burundi Pierre Nkurunziza ya baiwa ‘Yan kasar dake dauke da makamai wa’adin wata guda da su mika makamansu ga jami’an tsaro ko kuma su gamu da fushin hukuma.

Shugaban kasar Burundi, Pierre Nkurunziza.
Shugaban kasar Burundi, Pierre Nkurunziza. AFP PHOTO / LANDRY NSHIMIYE
Talla

Shugaban ya bayyana haka ne bayan shugaban hukumar kare hakkin Bil- Adama na Majalisar Dinkin Duniya ya shaida masa rahotan da suka samu na karuwar kashe kashen da ake samu a kasar.

Har ila yau, Shugaban Nkurunziza ya yi alkawarin hukunta Jami’an tsaron kasar da aka samu da laifin da azabtar da mutane ko kuma kashe su.

Nkurunziza ya ce bayan cikan wa’adin, duk wanda aka samu da makami ba tare da izini ba, zai gamu da fushin hukuma.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.