Jammeh ya yi wa Fursunoni da dama afuwa a Gambia
Shugaban kasar Gambia Yahya Jammeh ya yi wa mutane da dama da ke daure a gidan yari afuwa cikinsu har da wadanda aka yankewa hukuncin kisa, don murnar cikar shekaru 21 da darewarsa karagar mulkin kasar.
Wallafawa ranar:
Sai dai wannan afuwa ba ta shafi wadanda aka kama bayan da suka yi yunkurin kifar da gwamnatinsa ba a cikin watan Disambar bara, yayin da tsohon babban kwamandan askarawan kasar Janar Lang Tombong wanda aka sama da laifin cin amanar kasa a shekara ta 2010 da wasu mutane 7 za su ci moriyar wannan afuwa wadanda suka nemi kifar da gwamnatin shugaban a 2006.
A watan Maris ne aka yanke wa Sojojin hukuncin kisa wasu kuma hukuncin daurin rai da rai bayan kama su da laifun yunkurin juyin mulki.
Tun a 1994 Jammeh ke shugabanci a Gambia wanda ya dare kan madafan ikon kasar ta hanyar juyin mulki.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu