Isa ga babban shafi
Afrika ta tsakiya

MDD ta gargadi Afrika ta tsakiya akan ‘Yan gudun hijira

Majalisar Dinkin Duniya ta gargadi hukumomin kasar Jamhuriyar Afirka ta tsakiya kan daukar duk wani mataki na hana ‘yan gudun hijirar kasar shiga zaben da za a yi a watan Oktoba mai zuwa.

'Yan gudun Hijirar Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya
'Yan gudun Hijirar Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya REUTERS/Luc Gnago
Talla

Mai Magana da yawun hukumar ‘yan gudun hijira ta Majalisar Leon Dobbs ya ce ya zuwa yanzu ‘yan gudun hijira kusan 200,000 Musulmi ke zama a sansanin da ake kula da su, inda ya ke cewa hana su zabe zai yi matukar illa ga sahihancin zaben.

Majalisar tace akalla ‘yan kasar kusan 500,000 suka gudu daga kasar don tsira da rayukan su.
 

Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya ta fada cikin rikici ne tsakanin Mayakan Seleka musulmi da kuma anti balaka kirista a lokacin da Michel Djotodia na Seleka ya jagoranci hambarar da gwamnarin Francios Bozize.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.