Isa ga babban shafi
Masar

An kai harin Bom a ofishin jakadancin Italiya dake Masar

Yau Asabar mutum 1 ya rasa ransa, sakamakon wani Bom da ya fashe a ofishin jakadancin kasar Italiya dake birnin Alkahiran kasar Masar. Wakilin kamfanin dillancin labarun Faransa na AFP ya bayyana cewa fashewar, an dasa Bom a cikin wata mota da aka ajiye a kusa da ofishin, kuma lamarin yayi sanadiyyar lalacewa wani sashe na ofishin jakadancin. 

Shugaban kasar Masar, Abdel Fattah al-Sisi
Shugaban kasar Masar, Abdel Fattah al-Sisi REUTERS/The Egyptian Presidency/Handout via Reuters
Talla

Jami’an kula da lafiya a wajen, sun ce fashewar da ta faru da misalin karfe 6 da rabi na safe agogon kasar ta Masar, tayi sanadiyar raunata wasu ‘yan sanda 2 dake kula da wurin.
Tuni hukumomin birnin Rome suka yi Allah wadai da harin, sai dai sun ce harin bai shafi dan kasar ta Italiya.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.