Ebola
Wani kwararre yace mai yuwuwa cutar Ebola ta sake bayyana a duniya
Wani kwararren masani kan harkokin kula fa lafiya dan kasar Congo, Jean-Jacques Muyembe yayi gargadin cewa akwai yuwuwar cutar Ebola mai saurin kisa, zata sake far wa al’ummar duniya. Muyembe, wanda ke daya daga cikin masu bincike kan cutar ta Ebola, tun lokacin da aka fara gano ta a shekarar 1976, yayi gargadin cewa in Ebola tazo a wannan karon duk duniya zata yi ta’adi.Cutar Ebola, da zuwa yanzu aka shawo kanta, tayi sanadiyyar mutuwar fiye da mutane dubu 11 a kasashen Liberia, Saliyo da Guinea, tun lokacin data bayyana a baya bayan nan.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: