Cutar Sankarau ta kashe mutane 129 a Nijar
Hukumomin Jamhuriyyar Nijar sun ce cutar Sankarau ta kashe mutane 129 tun a watan Janairu, a yayin da aka soma rigakafin cutar a Makarantun Firamaren Yamai da Jihar Dosso a yau Juma’a. A cewar Ma'aikatar lafiya kimanin mutane 1,150 suka kamu da cutar ta Sankarau.
Wallafawa ranar:
Ministan kiwon lafiya Mano Aghali ya ce cutar na ci gaba da karuwa kuma za a soma rigakafin ne yau Juma’a, a makarantun Firamare.
A cewar Ministan kimanin mutane 1,150 suka kamu da cutar ta Sankarau.
Ministan ya ce tuni maganin Rigakafin ya iso Yamai babban birnin Jamhuriyyar Nijar, kuma suna fatar samun kawar da cutar a kasar.
Cutar Sankarau dai ta shafi Jihohin Nijar kusan guda 7, kamar yadda ministan ya tabbatar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu