Isa ga babban shafi
Afrika ta Kudu

Sarkin Zulu ya musanta zargin hura wutar kyamar baki

Sarkin Zulu da ke kasar Afirka ta kudu, Goodwill Zwelithini ya nesanta kansa da zargin tinzira al’ummar kasar su afkawa baki wajen kai musu hare hare, bayan zarginsa da hura wutar rikicin da ya janyo hasarar rayukan akalla mutane bakwai.

Sarkin Zulu Goodwill Zwelithini a wani taro a Durban
Sarkin Zulu Goodwill Zwelithini a wani taro a Durban REUTERS/Rogan Ward
Talla

Sarkin da ke jawabi ga dubban ‘yan kabilarsa a Durban, ya ce zargin da ya yi wa ‘yan kasashen waje kan matsalar da ake samu na tsaro a cikin kasar bai da nasaba da kai musu hari.

Sarkin ya ce ya yi kira ne ga ‘Yan sanda su inganta aikin tsaro.

Kasashe da dama dai sun yi allawadai da hare haren da mutanen Afrika ta kudu ke kai wa baki ‘yan kasashen waje.

Yanzu haka an cafke mutane sama da 300 bayan mutuwar mutane 7 a hare haren da ‘yan kasar suka kai wa baki da kasuwanci a Johannesburg.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.