'Yan Sanda sun tarwatsa matasan dake zanga zanga a Zamfara
A Jihar Zamfara Jami’an tsaro sun tarwatsa gungun wasu magoya bayan Jam’iyyar PDP wadanda suka nemi tayar da hargitsi a harabar ofishin hukumar zaben Jihar. Mutanen kasar na cigaba da dakon sakamakon zabe da yanzu haka kamar dai yada rahotani daga hukumar zaben kasar INEC ke bayana Jam'iyyar Apc a matsayi wace ta lashe zaben.
Wallafawa ranar:
Wannan kuma ya faru ne bayan da kafar yada labaran Jihar ta ruwaito cewa Jam’iyyar APC ce ta lashe zaben Gwamnan tun kafin hukumar INEC ta fadi sakamako.
Sai dai shugaban Jam’iyyar PDP a Jihar Senata Hassan Nasiha ya yi kira ga magoya bayansu da cewa su rungumi kaddara.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu