Nijar-Chadi
Dakarun Chadi sun kashe ‘Yan Boko Haram da dama
Rundunar sojin kasar Chadi ta ce dakarunta sun kashe mayakan Boko Haram da dama a musayar wutar da suka yi a garin Malam Fatori da suka kwato, amma Sojojin kasar 9 suka mutu.Kakakin rundunar Sojin Chadi Azam Bermandoa ya ce an kashe sojojinsu 9 yayin da 16 suka samu rauni amma sun kashe daruruwan ‘Yan Boko Haram.
Wallafawa ranar:
Talla
Dakarun Chadi da Nijar sun fatattaki Boko Haram a Malam Fatori da ke kan iyaka da Nijar, kuma Bermandoa ya ce sojojin sun kakkabe Boko Haram.
A watan Nuwamba ne Boko Haram ta kwace Malam Fatori, bayan ta yi ikirarin kafa sabuwar daula.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu