Kamaru-Najeriya
Boko Haram ta sace matafiya 20 a Kamaru
Kungiyar Boko haram ta sace wasu matafiya 20 a cikin wata motar safa da ke kasar Kamaru kuma mayakan na Boko Haram sun kashe 12 daga cikin su. Rahotanni sun ce an sace mutanen ne a karshen mako kamar yadda wani jami’in kungiyoyin fararen hula ya tababtar wa kamfanin dillancin labaran Faransa.
Wallafawa ranar:
Talla
Wata majiyar tsaro a Kamaru ta ce Mayakan Boko Haram sun kai motar mutanen hari ne a lokacin da suke kan hanya daga Koza zuwa Mora da ke yankin arewa mai nisa kusa da kan iyaka da Najeriya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu