Isa ga babban shafi
Tunisia

Jam’iyyar Essebsi ta yi ikirarin lashe zaben Tunisia

Beji Essebsi ya bayyana samun nasara a zaben shugaban kasa da aka gudanar a kasar Tunisia da yayin da shuagban kasa Moncef Marzouki ya yi watsi da ikrarin. Essebsi mai shekaru 88 ya yi jawabi gaban magoya bayansa 2,000 da suka hada gangami a Cibiyar Jam’iyar, yana mai bayyana godiya ga goyan bayan da suka ba shi.

Beji Caïd Essebsi na Tunisia
Beji Caïd Essebsi na Tunisia REUTERS/Anis Mili
Talla

Marzouki wanda shi ne shugaban rikon kwarya yace ikirarin Essebsi ya sabawa dimukuradiya.

Wannan ne karon farko da aka gudanar da zaben shugaban kasa a Tunisia bayan kawo karshen mulkin Zine Al Abidine Ben Ali.

A yau Litinin ne ake saran hukumar zaben kasar za ta bayyana sakamakon zaben.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.