Isa ga babban shafi

Cutar Ebola na raguwa a kasar Liberia

Hukumar lafiya ta duniya wato WHO tace ana samun raguwar mutanen da suke kamuwa da cutar Ebola a kasar Liberiya sai dai hukumar ta yi gargadin cewa har yanzu da sauran aiki a kokarin dakile cutar a kasar. A lokacin da yake yiwa maneman labari bayyani a geneva Mataimakin babban darakata hukumar Bruce Aylward yace wanna cigaba ba yana nufin an kawo karshan cutar ba, amma dai alamu ne na cewa an samu raguwar yaduwar cutar a liberia kuma da wanna za a iya kawo karshan cutar a kasar.Yace sai dai haka ba yana nufin mutane su saki jiki bane, a cewar shi dole a cigaba da taka tsantsan, hade da maida hankali wajen tsafta.Hukumar tace sabon adaddin mutane dake dauke da cutar a yanzu sun haura dubu 13, adaddin daya haura kididga da suka fitar a baya, kuma yawancinsu ‘yan asalin yammacin Afrika ne wadanda suka hada da kasar Guinea, Liberia, da Saliyo, inda cutar tafi tsanata a yanzu.A banagare guda kuma kasar Amurka ta kebe dakarunta da suka dawowa daga yankin Yammaci Africa, tsahon kwanaki 21 don kare kasar su daga cutar.Alyward yace yanzu babu mutum ko guda a kwance kan gadaje da ake kula da masu dauke da cutar a kasar, wannan dai na zuwa ne kwanaki biyu bayan shugaban Amurka Barak Obama, da kungiyar agaji ta Red Cross sun bada tabbacin samun cigaba a wajen yaki da cutar a kasar. 

Alamar hukumar lafiya ta duniya, WHO
Alamar hukumar lafiya ta duniya, WHO
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.