Mutane Biyar sun Mutu a harin Kano
Akalla mutane biyar suka mutu cikinsu har da wata karamar Yarinya a wani harin kunar bakin wake da aka kai a Birnin Kano a arewacin Najeriya, kamar yadda rundunar ‘Yan sandan Jahar ta tabbatar.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Kakakin rundunar ‘Yan Sandan Jihar Magaji Musa yace a wajajen misalin karfe 10 na dare ne aka kai harin Kunar bakin wake a Unguwar Sabon Gari kuma cikin wadanda suka mutu har da maharin da ya kai harin a cikin mota.
Harin kuma na zuwa ne bayan kammala zaben Kananan hukumomi inda Jam’iyyar Adawa ta APC mai adawa da PDP ta shugaba Goodluck Jonathan ta lashe kujerun shugabannin Kananan Hukumomin 44.
Rahoton Abubakar Isa Dandago daga Kano
A bara an taba kai hare haren bama bamai a Unguwar Sabon Gari a Kano inda mutane akalla 12 suka mutu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu