Biyan kudin fansho karshen kowane wata a jamhuriyar Nijar
Gwamnatin jamhuriyar Nijar ta kaddamar da wani shirin kidayar tsoffin ma’aikata na kasar domin samar da sabbin alkaluma da kuma soma biyan su kudin fansho a karshen kowane wata maimakon watanni uku uku.
Wallafawa ranar:
A jiya talata ne aka kaddamar da wannan aiki a duk fadin kasar, inda gwamnati ke cewa tana tunanin soma biyan kudin fanshon ne a karshen kowane wata domin ragewa tsoffin ma’aikatan irin waharhallun da suke fuskanta a rayuwarsu ta yau da kullum.
Da dama daga cikin tsoffin ma’aikatan da gidan rediyo Faransa ya tattauna da su kan wannan batu, sun bayyana goyon bayansu ga shirin saboda a cewarsu yana da muhimmanci.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu