Isa ga babban shafi
Nijar

Biyan kudin fansho karshen kowane wata a jamhuriyar Nijar

Gwamnatin jamhuriyar Nijar ta kaddamar da wani shirin kidayar tsoffin ma’aikata na kasar domin samar da sabbin alkaluma da kuma soma biyan su kudin fansho a karshen kowane wata maimakon watanni uku uku.

Mahamadou Issoufou, shugaban jamhuriyar Nijar
Mahamadou Issoufou, shugaban jamhuriyar Nijar France 24
Talla

A jiya talata ne aka kaddamar da wannan aiki a duk fadin kasar, inda gwamnati ke cewa tana tunanin soma biyan kudin fanshon ne a karshen kowane wata domin ragewa tsoffin ma’aikatan irin waharhallun da suke fuskanta a rayuwarsu ta yau da kullum.

Da dama daga cikin tsoffin ma’aikatan da gidan rediyo Faransa ya tattauna da su kan wannan batu, sun bayyana goyon bayansu ga shirin saboda a cewarsu yana da muhimmanci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.