Ambaliya ta yi barna a Nijar
Mutane Takwas aka ruwaito sun mutu sakamakon ambaliyar ruwa a garin Maradi da Agadez da Damagaram a Jamhuriyyar Nijar. Mahukuntan kasar sun ce cikin wadanda suka mutu akwai yara kanana guda bakwai yayin da mutane kusan 2,000 suka rasa matsuguninsu.
Wallafawa ranar:
Rahotanni sun ce matsalar tafi kamari a Maradi, inda mutane suka samu mafaka a makarantu.
Gidan Rediyon amfani ya ruwaito cewa akwai yara ‘Yan mata guda biyu da suka mutu a garin Damagaran, yayin da kuma a garin Agadez aka samu wata yarinya mai shekaru biyar da ta mutu bayan gini ya rubta da ita sakamakon ambaliyar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu