Matsalar tsaro a Najeriya barazana ce ga kasashen Afrika, inji shugaban Ghana
A lokacin da ya kawo ziyara kasar Faransa, Shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama yace mastalar tsaro a Najeriya barazana ce ga kasar Ghana, yana mai bayyana fatar gwamnatin Najeriya za ta dauki matakan magance matsalar kafin ta shafi sauran kasashen da ke makwabtaka da ita.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
“Matsalar tsaro barazana ce ga Ghana, domin Najeriya babbar kasar ce a yammacin Afrika ta fannoni da dama” a cewar shugaba Mahama.
Bayan ganawa da shugaba François Hollande, Mista Mahama ya jinjinawa gudunmuwar da Faransa ke ci gaba da bayar wa a rikicin arewacin Mali.
Shugaban na Ghana yace matsalar mayaka babbar barazana ce ga kasashen yammacin Afrika.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu