Isa ga babban shafi
Najeriya

Clinton ta yi kiran aiwatar da sabbin sauye sauye a Najeriya

Sakatariyar Harkokin wajen Amurka, Hillary Clinton, ta bukaci shugabanin Najeriya aiwatar da sabbin sauye sauyen da za su fitar da al’ummar kasar daga matsanancin talauci, abinda tace shi ya haifar da matsalar tsaron da ya addabi kasar yanzu haka.

Sakatariyar Harakokin Wajen Amurka Hillary Clinton tare da Goodluck Jonathan a ziyarar da ta kai a Najeriya
Sakatariyar Harakokin Wajen Amurka Hillary Clinton tare da Goodluck Jonathan a ziyarar da ta kai a Najeriya REUTERS/Jacquelyn Martin/Pool
Talla

Bayan ganawa da shugaba Goodluck Jonathan, da kuma hafsoshin tsaro, Clinton tace Najeriya tana da hanyoyin bunkasa tattalin arzikin kasa da dama, amma hakan ba zai samu ba, sai an samarwa daukacin ‘Yan kasar madafa, kuma an yi yaki da talaucin da ya addabi al’umma.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.