Isa ga babban shafi
Jamhuriyyar Congo

An sake samun tsaikun sakamakon zabe a Jamhuriyyar Congo

Hukumar zaben kasar Jamhuriyar Demokradiyyar Congo ta sake dage bayar da sakamakon zaben shugaban kasa da aka gudanar, har zuwa yau juma’a.

Wani dan Kasar Congo yana karanta Jarida mai dauke da kanun labarin zaben Jamhuriyyar Congo tsakanin  Joseph Kabila da Etienne Tskisekedi"
Wani dan Kasar Congo yana karanta Jarida mai dauke da kanun labarin zaben Jamhuriyyar Congo tsakanin Joseph Kabila da Etienne Tskisekedi" Daniel Finnan
Talla

A ranar 28 ga watan Nuwamba ne aka gudanar da zaben shugaban kasar, da farko an shirya bayar da sakamakon zaben a ranar talata daga bisani kuma aka dage zuwa jiya Alhamis, yanzu kuma hukumar zaben tace sai a yau Juma’a ne za’a samu sakamakon bayan ta kammala diba sahihancin sakamakon..

Kafin bayyana sakamakon, sai kotun kolin kasar ta yi nazari akai, tare kuma bayyana wanda ya lashe a ranar 17 ga wannan watan.

Wannan matakin ya sake cusa shakku da tsoron sake samun aukuwar tashin hankuli a cikin kasar inda ake zaman dar-dar tsakanin magoya bayan ‘Yan adawa da gwamnatin kasar.

Sakamakon farko da aka fitar ya nuna shugaba Joseph Kabila ne ke jagoranci da yawan kuri’u kashi 48.9, sai kuma abokin hamayyarsa Etienne Tshisekedi day a samu yawan kuri’u 33.3.

‘Yan adawa a kasar sun yi na’am da tsaikun da aka samu na bayyana sakamakon zaben, domin suna ganin hukumar zaben tana kokarin kamanta adalci ne a zaben, amma Jam’iyyar Madugun adawa Etienne Tshisekedi ta yi barazar kalubalantar zaben idan har aka bayyana shugaba Kabila ne ya lashe zaben.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.