Isa ga babban shafi
Jamhuriyyar Congo

An Samu jinkirin sakamakon zabe a Congo

Hukumar Zabe a kasar Jamhuriyar Demokradiyar Congo, ta jinkirta bada sakamakon zaben kasar da hukuamr ta yi alkalin sanarwa a jiya, sa’oi 48 bayan kammala zaben saboda abinda ta kira matsalolin da fuskanta.

Masu zanga-zanga a birnin Toronto kasar Amurka dauke da tutar mai sakon neman 'Yancin Congo kan zaben shugaban kasa da aka gudanar a Jamhuriyyar Demokradiyyar Congo
Masu zanga-zanga a birnin Toronto kasar Amurka dauke da tutar mai sakon neman 'Yancin Congo kan zaben shugaban kasa da aka gudanar a Jamhuriyyar Demokradiyyar Congo REUTERS/Mark Blinch
Talla

Sakamakon da hukumar ta bayar jiya, ya nuna cewar shugaba Joseph Kabila na da kashi 46, yayin da Etienne Tshisekedi yana da kashi 36, daga kashi biyu bisa uku na kuri’un da aka kirga, sai dai ana fargabar tashin hankali.

A lokacin da yake ganawa da kamfanin Dillacin labaran Reuters, kakakin hukumar zaben kasar Laurent Ndaye yace akwai akwai sauran sakamakon da basu samu ba daga wasu mazabu kuma hakan ne yasa aka samu tsaikun bayyana sakamakon zaben.

Sai dai ‘Yan adawa sun ce zasu yi watsi da sakamakon zaben bayan nuna shugaba Kabila ne kan gaba, Al’amarin da ke iya jefa kasar cikin rikici.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.