China da Rasha sun dakile sanarwa kan Rohingya
Kasashen China da Rasha sun dakatar da yunkurin fitar da wata sanarwa wadda za ta kunshi matsayin Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya kan azabar da sojoj ke gana wa al’ummar Rohingya da ke Myanmar
Wallafawa ranar:
Sojojin dai sun kwashe watanni hudu suna kisa da fyade a Rohingya, abin da masu bincike na hukumar kare hakkin dan Adam ta Majalisar Dinkin Duniya suka ka ce ka iya zama laifukan yaki.
Jakadan Birtaniya a kwamitin sulhun, Mathew Rycroft ya shaida wa manema labarai cewa, sun gaza cimma matsaya kan fitar da sanarwar wadda China da Rasha da ke da kujerun din-din-din suka dakatar da ita.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu