Isa ga babban shafi
Japan-Korea ta Arewa

Japan zata girke makaman kariyar harin Koriya ta Arewa

Ministan tsaron kasar Japan Naoki Tanaka, ya bada umurni girke makaman kariya daga makamai masu linzami da kasar Koriya ta Arewa zata harba masu cin dogon zango a watan gobe.

Wani makamin roka kirar  H-2A da kasar Japan ta kaddamar a  Tanegashima kudu maso yammacinTanegeshima,  kusa da birnin Tokyo
Wani makamin roka kirar H-2A da kasar Japan ta kaddamar a Tanegashima kudu maso yammacinTanegeshima, kusa da birnin Tokyo Reuters
Talla

A Yau Juma’a ne, minista Tanaka ya bayyana wa manema labarai, a Tokyo babban birnin kasar, inda ya ce jiragen ruwan yaki zasu dauk makaman kariyar, da zasu wargaza makamai masu linzamin na kasar koriya ta Arewa.

Cikin watan gobe kasar ta Koriya ta Arewa ta ce zata harba tauraron dan adam sararin samaniya, amma duk wani umurni kakkabo rokar kasar, sai ya samu amincewar Fira ministan kasar ta Japan Yoshihiko Noda.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.