A ranar 17 ga watan Yuli ne Kotun hukunta manyan laifuka ta ICC ta cika shekaru 15 da kafuwa wacce aka kafa domin hukunta laifukan yaki na bai daya a duniya. Wannan kuma na zuwa a dai dai lokacin da shugabannin kasashen Afrika ke zargin kotun ta fi mayar da hankali wajen farautarsu. a Cikin shirin Duniyarmu A Yau, Bashir Ibrahim Idris tare da abokan shirinsa sun tattauna akan wannan batu.