'Yan kwantenar tashar Apapa na kokawa kan cin hanci a Najeriya
Wallafawa ranar:
Kunna - 02:53
A Najeriya, yayin da gwamnatin kasar ke cewa tana yaki da cin hanci da rashawa a kasar, ‘yan kwantena da direbobin dakon kaya na kokawa da yadda lamarin ya yi musu katutu a tashar jiragen ruwan Apapa dake birnin Lagas.‘Yan kwantenar dai sun ce suna kashe akalla kimanin Naira dubu 185 kafin mota daya ya shigar tashar don daukar kaya, matakin da masharhanta ke ganin wata kila ke janyo hauwahawan farashin kayayyaki a kasar.Alhaji Auwalu, wani mai harkokin kwantenar a tashar ta Apapa, a Zantawarsa da Ahmad Abba ya ce, lamarin yafi karfin yadda ake tunani. Ku latsa alamar sauti dake kasa domin sauraro.