Gwamnatin tarayyar Najeriya na shirin ciyo bashin sama da Dalar bilyan biyu daga bankin duniya kudaden da za ta yi amfani da su domin raya yankin arewa maso gabashin kasar mai fama da ayyukan Boko Haram, Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, wanda ke jawabi jim kadan bayan ya gana da jami’an bankin na duniya a birnin Washington inda yake gudanar da ziyarar aiki, ya ce yankin na arewa maso gabashin Najeriya ya tagayyar ainun, kuma yana bukatar a sake gina shi a cikin gaggawa.Alhaji Kiyari Idris Abubakar, daya daga cikin shugaban al’umma a wannan yanki, ya bayyana wa Abdulkarim Ibrahim Shikal yadda suke fatan a yi amfani da wadannan kuadaden.
Sauran kashi-kashi
-
Bashir Dan-Malam kan karancin man fetur a sassan Najeriya
Rahotanni daga sassan arewacin Najeriya na nuna cewar an fara samun karancin mai a gidajen mai, abinda ya sa wasu masu man suka kara farashin da suke sayar da kowacce lita.25/04/202403:16 -
Arewa maso Yammacin Najeriya ne mafi hatsari saboda matsalar tsaro - Bincike
Kungiyar 'Global Rights' ta bayyana yankin arewa maso yammacin Najeriya a matsayin mafi hadari, saboda yadda 'yan bindiga ke kisa da take hakkin Bil Adama ba tare da kaukautawa ba.18/04/202403:16 -
Kuskure ne a yi tunanin ɗagawar darajar naira ba zai ɗore ba - Dakta Kurfi
Darajar Naira na cigaba da ɗagawa a Najeriya tare da saukar farashin wasu kayayyakin abinci a wasu kasuwannin ƙasar, abinda ya sa wasu tunanin cewar tasirin saukar Dalar ne ya sanya wasu kayayyakin suka fara sauka.17/04/202403:19 -
Tattaunawa da Sanata Ikira Aliyu Bilbis kan tsaro a jihar Zamfara
Hukumomi a Najeriya daga matakin jiha zuwa na kasar baki ɗaya na daukar matakai daban daban wajen samar da zaman lafiya a jihar Zamfara, amma har ya zuwa wannan lokaci ba'a kai ga cimma biyan bukata ba.16/04/202403:26 -
Yadda rayuwa ta kasance bayan da muka faɗa hannun mayakan Boko Haram - Maryama
A ranar Lahadi, 14 ga watan Afrilun nan aka cika shekaru 10 da sace dalibai mata na makarantar sakandaren Chibok sama da 250 da mayakan Boko Haram suka yi a jihar Borno.15/04/202403:17