Isa ga babban shafi

Faransa tace akwai alamun samun nasara a tattaunawar nukiliyar Iran

Kasar Faransa tace akwai alamar samun nasara a tattaunawar da ake yi a Vienna domin warware takaddama akan shirin nukiliyar Iran.

Shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron
Shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron AFP - KAY NIETFELD
Talla

Wani jami’i a fadar shugaban Faransa yace duk da yake akwai batutuwa masu nauyi da ba’a kaima cimma yarjejeniya akai ba dangane da cirewa kasar Iran takunkumi, akwai alamar dake nuna haske dangane da taron dake gudana.

Jami’in yace shugaban Faransa Emmanuel Macron a cikin kwanaki masu zuwa zai tattauna da takwaran sa na Iran Ebrahim Raisi ta waya dangane da tattaunawar da ake gudanarwa.

Tutar kasar Iran
Tutar kasar Iran © 路透社图片

Wadannan kalamai sun sha ban ban da wadanda ministan harkokin wajen Faransa Jean Yves Le drian yayi a makon jiya, inda yake korafi akan tsaikon da ake samu wajen tattaunawar. Jagoran kungiyar kasashen Turai wajen tattaunawar Enrique Mora yace an dakatar da tattaunawar yau juma’a domin bada damar daukar wasu matakai kafin ci gaba a makon gobe.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.