Mutane dubu 500 ne suka mutu bayan kamuwa da Covid 19 a Brazil
Bresil ce kasa ta biyu a Duniya bayan Amurika inda aka fi samu yawan mutane da suka mutu bayan kamuwa da cutar Covid 19.Akalla mutane dubu 500 ne suka mutu a dan tsakanin nan,wanda ke kara tabbatar da yawaitar mamata a kasar bayan harbuwa da kwayar cutar Covid 19.
Wallafawa ranar:
Alkaluman baya-baya nan daga ofishin Ministan lafiya na kasar na bayyana cewa kusan mutane 2.301 ne suka mutu cikin sa’ao’I 24.
Kasar dake da yawan al’uma da suka kai milyan 212,a jiya asabar ka dai mutane dubu 82.288 ne suka kamu da cutar covid 19.
Shugaban kasar Jair Bolsonaro wanda a fusace ya dinga furta kalamai marasa dadi,tareda danganta yan kasar da yan madigo na fuskantar suka daga yan kasar yanzu haka.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu