Isa ga babban shafi
Birtaniya

Kamfanin Google ya kare kansa daga zargin kin biyan kudin haraji

Shugaban Kamfanin Google Eric Schmidt ya kare kamfanin Yanar Gizon na kasar Amurka kan zargin kin biyan Haraji ga kasar Birtaninya. Shugaban Kamfanin dai ya kare zargin da ake yiwa Kamfanin ne a wani Rubutun da yayi a wata Jarida da ake kira Observer, inda yake cewar a kowane lokaci Google nada anniyar yin abinda ya yi dai dai da doka ne, ba yi mata karan tsaye ba.  

Kamfanin Google
Kamfanin Google Reuters
Talla

Ya kara da cewar Kamfanin na Google, ya kuma biya wasu kayyadaddun Kudade ga gwamnatin kasar Birtaniya a cikin Gida.

Idan ana iya tunawa a Satin daya gabata ne Shugabar wani Kwamitin kula da al’amurran da suka shafi al’umma na Majalisar kasar Birtaniya Margret Hodge ta bayyana Kamfanin Google a matsayin “Takadari” da baya son biyan haraji, a lokacin da mataimakin shugaban Kwamitin ke karba tambayoyin kwamitin.

Ta ce Google na tara kudi da suka kai Biliyan 4.9 na kuding Ingila a kowace shekara, amma kuma ya biya milliyan shuda ne kurum a shekarar 2011.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.