Isa ga babban shafi

City da Madrid sun lashe wasanninsu a gasar zakarun Turai

A jiya Talata ne aka dawo gasar lashe kofin zakarun Turai, inda aka fara wasannin zageye na biyu na gasar.

'Yan wasan Manchester City a lokacin da su ke murnar cin kwallo a karawarsu da Copenhagen.
'Yan wasan Manchester City a lokacin da su ke murnar cin kwallo a karawarsu da Copenhagen. AFP - JONATHAN NACKSTRAND
Talla

A wasannin da aka yi, Manchester City da ke  kare kambun ta kara da FC Copenhagen, inda ta samu nasara da ci 3-1, lamarin da ke nuna cewar kungiyar ta ci gaba da kokarinta na kare kambun wannan gasa da ta lashe a kakar wasan bara.

Kevin de Bruyne ne ya fara jefa kwallo a raga, kafin daga bisani Magnus Mattsson ya farke kwallon, bayan da mai tsaron ragar City Ederson yayi kuskuren bada kwallo.

Sai dai kafin a tafi hutu rabin lokaci, Bernardo Silva ya sake jefa kwallo wacce ta bai wa City damar shiga gaba a wasan.

A dayan wasan kuwa, Real Madrid ta samu nasara a wasan da ta yi da RB Leipzig.

Dan wasan gaba na tawagar Real Madrid Brahim Diaz, a lokacin da ya zura kwallo a karawar da suka yi da RB Leipzig.
Dan wasan gaba na tawagar Real Madrid Brahim Diaz, a lokacin da ya zura kwallo a karawar da suka yi da RB Leipzig. REUTERS - LISI NIESNER

Dan wasan tsakiya na kungiyar Brahim Diaz ne ya ci wa kungiyar kwallo daya tilo, da ta share mata hanyar zuwa matakin daf da na kusa da na karshe a karo na 12 cikin kaka 14.

A ranar Laraba 6 ga watan Maris ne za a yi kara wa ta biyu tsakanin Manchester City Copenhagen, sai kuma Real Madrid da RB Leipzig.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.