Isa ga babban shafi

Zakarun Turai: City za ta buga da Copenhagen, Arsenal da Porto

Mai rike da kofin zakarun nahiyar Turai, Manchester City za ta fafata da Copenhagen a matakin kungiyoyi 16 a gasar, a yayin da Arsenal ta barje gumi da FC Porto ta kasar Portugal.

Kwallon kafa ta gasar EUFA.
Kwallon kafa ta gasar EUFA. © REUTERS - PHIL NOBLE
Talla

Copenhagen ta kasar Denmark, wadda ta lashe gasar kasar, ta kai wannaan matsayi ne a karon farko tun bayan shekarar 2011.

Za a buga Zubin farko na wannan gasa ne a ranakun 13 da 14 da 20 da 21 ga watan Fabrairun shekarar 2024, kana a yi zubi na biyu a ranakun 12 da 13 ga watan Maris.

City da Arsenal duk za su buga wasanninsu na farko ne a gida.

Real Madrid, wadda sau 14 ta lashe wannan kofi na zakarun nahiyar Turai za ta fafata da RB Leipzig, a yayin da Inter Milan, wadda ta kammala gasar shekarar da ta  gabata a matsayi na biyu za ta buga da Atletico Marid, a yayin da Bayern Munich za ta kara da Lazio.

Za a yi wasan karshe na wannan gasa ne a filin wasa na Wembley a Ingila, a ranar 1 ga watan Yuni.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.