Isa ga babban shafi

Kamaru tasha da kyar a hannun Guinea bayan da suka tashi 1-1

Tawagar kasar Guinea a gasar lashe kofin Afrika da ke gudana a Ivory Coast, ta rike takwararta ta Kamaru 1 da 1 a wasan farko na rukunin C da suka fafata a yammacin Litinin din nan.

Dan wasan baya na tawagar Guinea Sekou Sylla tare da dan wasan gaba na tawagar Kamaru Franck Magri a lokacin wasansu na rukunin C da aka yi a ranar Litinin 15 ga watan Janairun 2024.
Dan wasan baya na tawagar Guinea Sekou Sylla tare da dan wasan gaba na tawagar Kamaru Franck Magri a lokacin wasansu na rukunin C da aka yi a ranar Litinin 15 ga watan Janairun 2024. AFP - ISSOUF SANOGO
Talla

Guinea wacce ke mataki na 80 a jadawalin da Hukumar Kwallon kafa ta dDuniya FIFA ta fiar ce dai ta fara jefa kwallo a ragar Kamaru ta hannun Mohamed Bayo, kafin Frank Magri ya farke mata.

Tawagar ta Kamaru ta yi yunkurin kara kwallo, sai dai ta fuskanci turjiya daga wajen mai tsaron ragar Guinea Ibrahim Kone.

Wannan kunnen dokin ya sake bai wa Senegal damar jagorantar rukunin, ganin yadda ita kadai ce ta samu maki da kuma kwallo 3.

Dan wasan Guinea Mohamed Bayo, tare da sauran abokan wasansa, lokacin da suke murnar zura kwallo a ragar Kamaru.
Dan wasan Guinea Mohamed Bayo, tare da sauran abokan wasansa, lokacin da suke murnar zura kwallo a ragar Kamaru. AP - Sunday Alamba

A wasan gaba, Kamaru za ta kara ne da Senegal ita kuma Guinea ta barje gumi da Gambia.

Sakamakon wasan dai ya ci gaba da bada mamaki a gasar lashe kofin Afrika da ke gudana a Ivory Coast, ganin yadda kasashen da suka yi suna a fagen kwallon kafar nahiyar ke shan mamaki a hannun masu tasowa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.