Na yafe wa dan majalisar Ghana da ya mini shagube - Maguire
Dan wasan bayan Manchester United, Harry Maguire, ya amince ya yafe wa wani dan majalisar dokokin kasar Ghana da ya yi masa shagube yayin zaman majalisar a shekarar bara.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Dan wasan wanda ya wallafa a shafinsa na X Wanda aka fi sani da Twitter, ya ajiye wa dan majalisar sakon cewa sai mun hadu a filin wasa na Old Trafford.
Shi dai Isaac Adongo a yayin zaman mahawara kan kasafin kudin kasar da aka gudanar a shekarara 2022, an jiyo yana kalamai marasa dadi ga Maguire, inda yake danganta koma bayan tattalin arzikin kasar da ake samu da irin rawar da dan wasan ke takawa a Manchester United.
Sai dai kuma, a ranar Talata aka sake jiyo shi wannan dan majalisa na neman afuwar Maguire, inda har ma ya bayyana shi a matsayin zakakurin dan wasa da ke bayar da gudun mowa ainun don ganin cewa kungiyar ta kai ga gaci.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu