Isa ga babban shafi

An nemi sayen tikitin gasar cin kofin duniya ta bana kusan miliyan 24 - FIFA

Hukumar FIFA ta ce an nemi tikitin shiga filaye don kallon wasannin gasar cin kofin duniya miliyan 23 da dubu 500, yayin da ya rage  kasa da watanni 7 babbar gasar ta fara gudana a kasar Qatar.

Fasalin daya daga cikin filayen da za su karbi bakuncin wasannin gasar cin kofin duniya ta 2022 da za ta gudana a kasar Qatar.
Fasalin daya daga cikin filayen da za su karbi bakuncin wasannin gasar cin kofin duniya ta 2022 da za ta gudana a kasar Qatar. REUTERS - KAI PFAFFENBACH
Talla

Rahoton na FIFA, ya ce bukatar tikitan kallon wasannin na gasar cin kofin duniya ya fi yawa daga kasashen Argentina, da Brazil, da Ingila, da Faransa, da Mexico. Sai kuma mai masaukin baki, wato kasar ta Qatar, da Saudiya da kuma Amurka.

Shugaban hukumar kwallon kafa ta duniya Gianni Infantino.
Shugaban hukumar kwallon kafa ta duniya Gianni Infantino. REUTERS - KAI PFAFFENBACH

Hukumar ta FIFA ta kara da cewar, farashin tikitin gasar cin kofin duniyar ta bana, ya karu da kusan kashi 30 cikin 100 idan aka kwatanta da na gasar da Rasha ta karbi bakunci a shekarar 2018.

Tikiti mafi arha a bana dai na 'yan Qatar ne da kuma bakin-hauren da ake aiki a kasar, wadanda za su biya dala 10 kacal don kallon wasannin zagayen farko na matakin rukuni.

Sai dai fa a wasan karshe, farashin tikiti mafi tsada ya zarce da dala dubu 1,600, kwatankwacin naira 664,304 a kudin Najeriya, abinda ke nufin an samu karin kashi 45 cikin 100 kan farashin da aka gani a shekarar 2018.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.