Isa ga babban shafi

Liverpool na gab da kaiwa wasan karshe na gasar zakarun Turai

Liverpool na gab da zuwa wasan karshe na gasar cin kofin zakarun Turai karo na uku a cikin shekaru biyar, bayan da ta samu nasara kan Villarreal da 2-0, a wasan farko na zagayen kusa da na karshe da suka fafata a filin wasa na Anfield a ranar Laraba.

Sadio Mane yayin jefa kwallo ta biyu a ragar Villareal yayin karawarsu ta farko a zagayen wasan kusa da na karshe a gasar zakarun Turai.
Sadio Mane yayin jefa kwallo ta biyu a ragar Villareal yayin karawarsu ta farko a zagayen wasan kusa da na karshe a gasar zakarun Turai. REUTERS - PHIL NOBLE
Talla

Liverpool ta ci kwallayen biyu ne cikin mintuna biyu, ta hannun ‘yan wasanta Jordan Henderson da Sadio Mane.

A yanzu haka dai a iya cewar kungiyar ta Liverpool na da damar lashe jumillar kofuna har guda hudu a kakar wasa ta bana, domin kuwa bayan fatan kaiwa wasan karshe na gasar zakarun Turai, tazarar maki 1 kacal Manchester City ta baiwa Liverpool din a gasar Firimiyar Ingila wadda ya rage wasanni 4 a kammala ta.

Tuni dai Liverpool din ta lashe kofin Carabao. Akwai kuma gasar cin kofin kofin FA, da za ta fafata wasan karshenta ta Chelsea a ranar 14 ga watan Mayu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.