Isa ga babban shafi
Wasanni

An gano dalilin da ya sa Alkali tsayar da wasan Tunisia da Mali sau biyu

Bayan shafe kwanaki ana cece-kuce akan Janny Sikazwe, alkalin wasa dan kasar da ya jagoranci wasan da aka buga tsakanin Tunisia da Mali a ranar Laraba, an gano dalilinsa na busa usur din kawo karshen fafatawar kafin lokaci ya cika har sau biyu.

Alkalin wasa Janny Sikazwe yayin musayar yawu da mai horas da 'yan wasan Tunisia.
Alkalin wasa Janny Sikazwe yayin musayar yawu da mai horas da 'yan wasan Tunisia. © Reuters
Talla

A ranar ta Laraba dai, Sikazwe ya fara kawo karshen wasan Tunusia da Mali ne a minti na 85, da kuma minti na 89, abinda ya janyo hayaniya daga bangaren tawagar kwallon kafar Tunisia.

Sai dai a yayin da yake karin bayani akan lamarin, shugaban alkalan wasan da ke alkalanci a wasannin gasar cin kofin Afirka, Essam Abdel-Fatah, ya ce alkali Janny Sikazwe yayi fama ne da matsalar tsananin zafin da makinsa ya kai 34 a ma’aunin Celcius abinda ya haifar da karancin ruwa a jikinsa.

Abdel-Fatah ya kara da cewar ko bayan Karkare wasan da Mali ta doke Tunisia da 1-0 a filin was ana Limbe da ke Kamaru, sai da aka gaggauta garzawaya da Alkali Sikazwe asibiti domin ceto lafiyarsa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.